Gabatarwa
1. Na gode Jallah don Shi ne yake yi min
Baiwa ta komai ba hani za ya min
2. Ƙarin salati ga Nabiyyi Mustafa
Da Alihi Sahabbai nasa ba ƙwafa
Farkon Wajibi a Kan Bayi
3. Sanin Ilahu wajibinka bawa
Na farko in ka ƙi ka zamto gawa
4. Ko numfashinka ya cike Samaniya
Izza gare ka kan Ƙassai da Maliya
5. "Wa Ma khalaqqul Jinnah" Allah ya ce:
"Wal Insa" sai bauta ka san ka dace.
Wanene Bawa?
6. Duk wani mahluki idonka ke gani
Ƙira shi bawa duk ficensa ya sani
7. Mai hankalinsu akasinsu mumini
Ko kafiri, da fajiri, da ƙanƙani
8. Mana ta bawa wata mai biyayya
Ga Jallah donSa kullum ke biyayya
9. Ba shi da tsoron ya wuce ƙiyama
Ba shi da haushin madara da nama.
Ma'anar Bauta
10. Bauta sanin abin da Jallah ya ka so
Ya lamance na aiki koda ba ka so
11. Na zahiri da baɗini duk ta haɗa
Da ƙauracewa kishiyarta an faɗa
12. Aikin ibada da cikar soyayya
Ke yinsa bawa babu yin jayayya
13. Har risinawarsa cikar bautarsa
Da so da ƙi don Jallah ne nufinsa.
Sharuɗan Bauta
14. Kyan niyya ayyukansa sa ikhlasi
Biyayya gun Manzo da ba iflasi
15. Addini wasu sunka ce ƙwazonsa
Allah roƙonmu gunka ne baiwarsa.
Matakan Addini
16. Dinin Islama na da matakai uku
Ga jerin nan gare ka tamkar ranaku
17. Islamu Addinin Ilahu yai gaba
Birni da ƙauye ba kamarsa cigaba
18. Imani shi ne na biyunsu ka ji
Lurarka dai ta zam gare shi ba ji
19. Ihsani shi ne na uku ba tantama
Shi ne ya zo a ƙoli ba mai gardama.
©Ibrahim Lawal Soro
09. 09. 2022 CE.
No comments:
Post a Comment